Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -

Zabura 67 - Littafi Mai Tsarki


Waƙar Miƙa Hadaya ta Godiya

1 Ka yi mana jinƙai, ya Allah, ka sa mana albarka, Ka dube mu da idon rahama,

2 Domin dukan duniya ta san nufinka, Dukan sauran al'umma kuma su san cetonka.

3 Da ma dukan mutane su yabe ka, ya Allah, Da ma dukan mutane su yabe ka!

4 Da ma sauran al'umma su yi murna, su raira waƙa ta farin ciki, Domin kana yi wa jama'a shari'a ta adalci, Kana kuma bi da dukan sauran al'umma.

5 Da ma dukan mutane su yabe ka, ya Allah, Da ma dukan mutane su yabe ka!

6 Ƙasa ta ba da amfaninta, Allah, wanda yake Allahnmu ne, ya sa mana albarka.

7 Allah ya sa mana albarka, Da ma dukan jama'a ko'ina su girmama shi.

@Bible Society of Nigeria 1979

Bible Society of Nigeria
ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:



ကြော်ငြာတွေ