Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -

Zabura 52 - Littafi Mai Tsarki


Hukuncin Allah da Alherinsa

1 Me ya sa kake fariya da muguntarka, Ya kai, babban mutum? Ƙaunar Allah tana nan a koyaushe.

2 Kana shirya maƙarƙashiya don ka lalatar da waɗansu, Harshenka kamar aska mai kaifi yake. Kana ƙirƙiro ƙarairayi kullum.

3 Kana ƙaunar mugunta fiye da nagarta, Kana kuwa ƙaunar faɗar ƙarya fiye da gaskiya.

4 Kana jin daɗin cutar mutane da maganganunka, Ya kai, maƙaryaci!

5 Don haka Allah zai ɓata ka har abada, Zai kama ka, yă jawo ka daga alfarwarka, Zai kawar da kai daga ƙasar masu rai.

6 Adalai za su ga wannan, su ji tsoro, Za su yi maka dariya, su ce,

7 “Duba, ga mutumin da bai dogara ga Allah Don ya sami zaman lafiyarsa ba. A maimakon haka, sai ya dogara ga wadatarsa. Yana neman zaman lafiyarsa ta wurin muguntarsa.”

8 Amma ni, kamar itacen zaitun nake, wanda yake girma kusa da Haikalin Allah, Ina dogara ga madawwamiyar ƙaunarsa har abada abadin.

9 Zan gode maka, ya Ubangiji, Saboda abin da ka aikata. Zan dogara gare ka, Sa'ad da nake sujada tare da jama'arka, Domin kai mai alheri ne.

@Bible Society of Nigeria 1979

Bible Society of Nigeria
ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:



ကြော်ငြာတွေ