Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -

Zabura 46 - Littafi Mai Tsarki


Allah ne Mafakarmu da Ƙarfinmu

1 Allah ne mafakarmu da ƙarfinmu, Kullum a shirye yake yă yi taimako a lokacin wahala.

2 Saboda haka ba za mu ji tsoro ba, Ko da duniya za ta girgiza, Duwatsu kuma su fāɗa cikin zurfafan teku,

3 Ko da a ce tekuna za su yi ruri su tumbatsa, Tuddai kuma su girgiza saboda tangaɗin tekun.

4 Akwai kogin da yake kawo farin ciki a birnin Allah, Da cikin tsattsarkan Haikali na Maɗaukaki.

5 Allah yana zaune cikin birnin, Ba kuwa za a hallaka birnin ba, faufau. Da asuba Allah zai kawo musu gudunmawa.

6 An kaɓantar da sauran al'umma, mulkoki suka girgiza, Allah ya yi tsawa, duniya kuwa ta narke.

7 Ubangiji Maɗaukaki yana tare da mu, Allah na Yakubu shi ne mafakarmu!

8 Zo ku ga abin da Ubangiji ya yi! Dubi irin ayyukan al'ajabi da ya yi a duniya!

9 Ya hana yaƙoƙi ko'ina a duniya, Yana karya bakkuna, yana lalatar da māsu, Yana ƙone karusai da wuta.

10 Ya ce, “Ku yi shiru, ku sani ni ne Allah, Maɗaukaki ne cikin sauran al'umma, Maɗaukaki kuma a duniya!”

11 Ubangiji Maɗaukaki yana tare da mu, Allah na Yakubu shi ne mafakarmu!

@Bible Society of Nigeria 1979

Bible Society of Nigeria
ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:



ကြော်ငြာတွေ