Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -

Zabura 20 - Littafi Mai Tsarki


Addu'ar Neman Nasara

1 Ubangiji ya amsa maka a ranar wahala! Allah na Yakubu ya kiyaye ka!

2 Ya aiko maka da taimako daga Haikalinsa, Ya kawo maka gudunmawa daga Sihiyona.

3 Ya karɓi hadayunka, Ya kuma ji daɗin dukan sadakokinka.

4 Ya ba ka abin da kake bukata, Ya sa dukan shirye-shiryenka su yi nasara.

5 Mu kuma, sai mu yi sowa ta farin ciki saboda ka ci nasara, Mu yi bikin cin nasara da ka yi, Da yabon Ubangiji Allahnmu. Allah ya amsa dukan roƙe-roƙenka!

6 Yanzu dai na sani Ubangiji yakan ba da nasara ga zaɓaɓɓen sarkinsa, Yakan amsa masa daga samaniyarsa mai tsarki, Da ikonsa mai girma yakan sa shi yă yi nasara.

7 Waɗansu ga karusan yaƙinsu suke dogara, Waɗansu kuwa ga dawakansu, Amma mu, ga ikon Ubangiji Allahnmu muke dogara!

8 Za su yi tuntuɓe su fāɗi, Amma mu za mu tashi mu tsaya daram!

9 Ka ba sarki nasara, ya Ubangiji, Ubangiji zai amsa mana sa'ad da muka yi kira.

@Bible Society of Nigeria 1979

Bible Society of Nigeria
ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:



ကြော်ငြာတွေ