Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -

Zabura 137 - Littafi Mai Tsarki


Kukan Isra'ilawa a Baƙuwar Ƙasa

1 A bakin kogunan Babila Muka zauna muka yi ta kuka, Sa'ad da muka tuna da Sihiyona.

2 A rassan itatuwan wardi da suke kusa da mu Muka rataye garayunmu.

3 Waɗanda suka kama mu suka sa mu mu yi waƙa, Suka ce mana, “Ku yi mana shagali Da waƙar da aka raira wa Sihiyona!”

4 Kaƙa za mu raira waƙar Ubangiji A baƙuwar ƙasa?

5 Da ma kada in ƙara iya kaɗa garaya, Idan na manta da ke, Urushalima!

6 Da ma kada in ƙara iya raira waƙa, Idan na manta da ke, Idan ban tuna ke ce Babbar abar farin ciki ba!

7 Ka tuna, ya Ubangiji, da abin da Edomawa suka yi, A ranar da aka ci Urushalima. Ka tuna da yadda suka ce, “A ragargaza ta har ƙasa!”

8 Babila, za a hallaka ki! Mai farin ciki ne shi wanda ya sāka miki Bisa ga abin da kika yi mana.

9 Mai farin ciki ne shi wanda zai kwashi jariranki Yă fyaɗa su a kan duwatsu!

@Bible Society of Nigeria 1979

Bible Society of Nigeria
ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:



ကြော်ငြာတွေ