Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -

Zabura 122 - Littafi Mai Tsarki


Yabon Urushalima

1 Na yi murna sa'ad da suka ce mini, “Tashi mu tafi Haikalin Ubangiji!”

2 Ga shi kuwa, mun iso, Muna tsaye a ƙofofin Urushalima!

3 Urushalima birni ce wadda aka maido ta yadda take dā, Da kyakkyawan tsari, a shirye!

4 A nan kabilai sukan zo, Kabilan Isra'ila, Domin su yi godiya ga Ubangiji, Kamar yadda ya umarce su.

5 A nan majalisu suke, Wurin da sarki yake yi wa jama'arsa shari'a.

6 Ku yi wa Urushalima addu'ar salama! “Allah ya sa masu ƙaunarki su arzuta!

7 Salama ta samu a garukanki, Da zaman lafiya kuma a fādodinki.”

8 Saboda abokaina da aminaina, Na ce wa Urushalima, “Salama a gare ki!”

9 Saboda Haikalin Ubangiji, Allahnmu, Ina addu'a domin ki arzuta.

@Bible Society of Nigeria 1979

Bible Society of Nigeria
ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:



ကြော်ငြာတွေ