1 Ka hanzarta, ya Allah, ka cece ni; Ya Ubangiji, zo da sauri ka taimake ni.
1 Ka cece ni, ya Allah! Ya Ubangiji, ka yi hanzari ka taimake ni!
Ka amsa mini da sauri, ya Ubangiji; ƙarfina ya ƙare. Kada ka ɓoye fuskarka daga gare ni in ba haka ba zan zama kamar waɗanda suka gangara zuwa rami.
Kada ka yi nisa da ni, ya Allah; zo da sauri, ya Allahna, ka taimake ni.
Ya Ubangiji, kada ka tsawata mini cikin fushinka ko ka hore ni cikin hasalarka.
Ka zo kusa ka kuɓutar da ni; ka fanshe ni saboda maƙiyana.