3 Bari mutane su yabe ka, ya Allah; bari dukan mutane su yabe ka.
3 Da ma dukan mutane su yabe ka, ya Allah, Da ma dukan mutane su yabe ka!
Kada ka bar waɗanda ake danniya su sha kunya; bari matalauta da mabukata su yabe sunanka.
Bari mutane su yabe ka, ya Allah; bari dukan mutane su yabe.
Ka ’yantar da ni daga kurkuku, don in yabi sunanka. Ta haka masu adalci za su taru kewaye da ni saboda alherinka gare ni.
Bari in rayu don in yabe ka, bari kuma dokokinka su raya ni.
Zan sa a tuna da kai a dukan zamanai; saboda haka al’ummai za su yabe ka har abada abadin.
ya ce, “Ɗan ƙaramin abu ne ka zama bawana don ka maido da kabilar Yaƙub ka kuma dawo da waɗannan na Isra’ilawan da na kiyaye. Zan kuma mai da kai haske ga Al’ummai, don ka kawo cetona zuwa iyakokin duniya.”
Saboda haka za a yashe Isra’ila har sai wadda take naƙuda ta haihu sauran ’yan’uwansa kuma sun dawo su haɗu da Isra’ilawa.