2 Taimakona zai zo daga wurin Ubangiji, wanda ya kafa sama da ƙasa.
2 Taimakona zai zo daga wurin Ubangiji, Wanda ya yi sama da ƙasa.
Gama ni ne Ubangiji Allahnka, wanda ya riƙe ka da hannun damana ya kuma ce maka, Kada ka ji tsoro; zan taimake ka.
Taimakonmu yana a sunan Ubangiji, Wanda ya yi sama da ƙasa.
Saboda haka muna iya fitowa gabagadi, mu ce, “Ubangiji ne mai taimakona; ba zan ji tsoro ba. Me mutum zai iya yi mini?”
Allah ne mafakarmu da ƙarfinmu, kullum yana a shirye yă taimaka a lokacin wahala.
Amma Ubangiji yana tare da ni kamar babban jarumi; saboda haka masu tsananta mini za su yi tuntuɓe ba kuwa za su yi nasara ba. Za su fāɗi su kuma sha mummunar kunya; ba za a taɓa manta da rashin bangirmansu ba.
Bari Ubangiji yă albarkace ku, shi Mahalicci sama da ƙasa.
“An hallaka ku, ya Isra’ila, domin kun tayar mini, kun tayar wa mai taimakonku.
A farko-farko, Allah ya halicci sama da ƙasa.