29 Sa’ad da Maryamu ta ji haka sai ta yi wuf ta tafi wurinsa.
29 Ita kuwa da jin haka, ta yi maza ta tashi ta nufi wurinsa.
Mutum yakan yi farin ciki a ba da amsar da take daidai, kuma ina misali a yi magana a lokacin da ya dace!
Zuciyata kan faɗa game da kai, “Nemi fuskarsa!” Fuskarka, Ubangiji, zan nema.
Kamar yadda ƙarfe kan wasa ƙarfe haka mutum kan koyi daga mutum.
Bayan ta faɗa haka kuwa, sai ta koma ta je ta kira ’yar’uwarta Maryamu a gefe. Ta ce, “Ga Malam ya zo, kuma yana kiranki.”
Yesu dai bai riga ya shiga ƙauyen ba tukuna, har yanzu yana inda Marta ta tarye shi.