39 Sai suka sāke yin ƙoƙari su kama shi, amma ya kuɓuce musu.
39 Sai suka sāke ƙoƙarin kama shi, amma ya fita daga hannunsu.
Da jin haka, sai suka yi ƙoƙari su kama shi, sai dai ba wanda ya taɓa shi, don lokacinsa bai yi ba tukuna.
Da jin haka sai suka ɗebo duwatsu don su jajjefe shi, amma Yesu ya ɓuya, ya fita daga filin haikali.
Waɗansu suka so su kama shi, sai dai ba wanda ya taɓa shi.
Sai Yahudawa suka sāke ɗebo duwatsu don su jajjefe shi,
Amma Farisiyawa suka fita suka ƙulla shawara yadda za su kashe Yesu.