Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




M.Sh 6:6 - Sabon Rai Don Kowa 2020

6 Waɗannan umarnai da nake ba ku a yau, za su kasance a zukatanku.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Littafi Mai Tsarki

6 Waɗannan kalmomi da na umarce ku da su a yau, za su zauna a zuciyarku.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




M.Sh 6:6
22 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Ku bar maganar Kiristi ta zauna a cikinku a yalwace yayinda kuke koya, kuna kuma yi wa juna gargaɗi da dukan hikima, da kuma yayinda kuke waƙoƙin zabura, waƙoƙi da waƙoƙin ruhaniya tare da godiya a zukatanku ga Allah.


“Ga alkawarin da zan yi da gidan Isra’ila bayan wannan lokaci,” in ji Ubangiji. “Zan sa dokata a tunaninsu in kuma rubuta ta a zukatansu. Zan zama Allahnsu, za su kuma zama mutanena.


Ka daure su a yatsotsinka; ka rubuta su a allon zuciyarka.


Saboda haka, sai ku riƙe waɗannan kalmomina gam a zukatanku da ranku; ku ɗaura su kamar alama a hannuwanku, da goshinku.


Dokar Allahnsa tana a cikin zuciyarsa; ƙafafunsa ba sa santsi.


Kun nuna cewa ku wasiƙa ce daga Kiristi, sakamakon hidimarmu, ba wadda aka rubuta da inki ba, sai dai da Ruhun Allah mai rai. Ba kuma a kan allunan dutse ba, sai dai a kan allunan zukatan mutane.


ya ce musu, “Ku riƙe dukan kalmomin da na furta muku a yau, don ku umarce ’ya’yanku su lura, su yi biyayya da dukan kalmomin wannan doka.


Na ɓoye maganarka a cikin zuciyata don kada in yi maka zunubi.


“Ku ji ni, ku da kuka san abin da yake daidai, ku mutanen da kuke da dokata a zukatanku. Kada ku ji tsoron ba’ar da mutane suke yi ko ku firgita saboda zargin da suke yi.


Amma irin da suka fāɗi a ƙasa mai kyau kuwa, su ne mutane masu kyakkyawar zuciya, mai kyau, da suka ji, suka riƙe, suka kuma jimre har suka ba da ’ya’ya.”


Ka dogara ga Ubangiji da dukan zuciyarka kada kuma ka dangana ga ganewarka;


Sai ya koma Nazaret tare da su, yana yi musu biyayya. Mahaifiyarsa kuma ta riƙe dukan waɗannan abubuwa a zuciyarta.


Umarnanka suna sa in zama mai hikima fiye da abokan gābana, gama kullum suna tare da ni.


Ina sha’awar aikata nufinka, ya Allahna; dokar tana cikin zuciyata.”


Muna ƙaunarku saboda gaskiyan nan, wadda take cikinmu za tă kuma kasance tare da mu har abada.


Saboda na zaɓe shi don yă umarci ’ya’yansa da iyalinsa a bayansa su kiyaye hanyoyin Ubangiji, ta wurin yin abin da yake daidai da kuma yin adalci, domin Ubangiji ya aikata abin da ya yi wa Ibrahim alkawari.”


Dukan dokokinsa suna a gabana; ban ƙi ko ɗaya daga umarnansa ba.


Ku rubuta su a kan madogaran ƙofofin gidajenku, da a kan ƙofofinku,


Da leɓunana na ba da labarin dukan dokokin da suka fito bakinka.


Na zaɓi hanyar gaskiya; na sa zuciyata a kan dokokinka.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ