7 Amma Yesu ya zo ya taɓa su ya ce, “Ku tashi, kada ku ji tsoro.”
7 Sai Yesu ya zo ya taɓa su, ya ce, “Ku tashi, kada ku ji tsoro.”
Har yanzu wannan wanda yana kama da mutum ya taɓa ni ya kuma ba ni ƙarfi.
Amma nan da nan Yesu ya ce musu, “Ku yi ƙarfin hali! Ni ne. Kada ku ji tsoro.”
Yayinda yake magana da ni, barci mai nauyi ya kwashe ni, da nake kwance rubda ciki. Sai ya taɓa ni ya kuma tashe ni tsaye.
Sa’ad da na gan shi, sai na fāɗi a gabansa sai ka ce matacce. Sai ya ɗibiya hannunsa na dama a kaina ya ce, “Kada ka ji tsoro. Ni ne Farko da kuma Ƙarshe.
Sai hannu ya taɓa ni ya sa makyarkyata a hannuna da ƙafafuna.
Yanzu ka tashi ka shiga cikin birnin, za a kuma gaya maka abin da dole za ka yi.”
A cikin tsoro, matan suka fāɗi da fuskokinsu a ƙasa, amma mutanen suka ce musu, “Me ya sa kuke neman mai rai a cikin matattu?
yayinda nake cikin addu’a, sai Jibra’ilu, mutumin nan da na gani a wahayin da ya wuce, ya zo wurina gaggauce wajen lokacin yin hadaya ta yamma.
Sa’ad da almajiran suka ji haka, sai suka fāɗi ƙasa rubda ciki, a firgice.
Da suka ɗaga kai, ba su ga kowa ba sai Yesu kaɗai.