8 Taron suka matso, suka ce roƙi Bilatus yă yi musu abin da ya saba yi.
8 Jama'a fa suka matso, suka fara roƙon Bilatus ya yi musu abin da ya saba yi.
A wannan irin Biki, gwamna yana da wata al’ada, ta sakin ɗan kurkuku guda wanda taron suka zaɓa.
Sai Yesu ya tashi daga nan ya tafi yankin Yahudiya, da kuma ƙetaren Urdun. Taron mutane suka sāke zuwa wurinsa, ya kuma koya musu kamar yadda ya saba.
Wani mutumin da ake kira Barabbas, yana a kurkuku, tare da waɗansu ’yan tawaye da suka yi kisankai a lokacin wani hargitsi.
Bilatus ya yi tambaya ya ce, “Kuna so in sakar muku Sarkin Yahudawa?”
Za ku turke dabbar har rana ta goma sha huɗu ga wata, wato, sa’ad da dukan taron jama’ar Isra’ila za su yanka ragunansu da yamma.