10 Da suna cikin gida kuma, sai almajiran suka tambayi Yesu game da wannan.
10 A cikin gida kuma sai almajiransa suka sāke tambayarsa wannan magana.
Suka iso Kafarnahum. Da yana cikin gida, sai ya tambaye su ya ce, “Gardamar me kuke yi a hanya?”
Da Yesu ya shiga gida, almajiransa suka tambaye shi a ɓoye, suka ce, “Me ya sa ba mu iya fitar da shi ba?”
Lokacin da yake shi kaɗai, Sha Biyun, da kuma waɗanda suke kewaye da shi, suka tambaye shi game da misalan.
Domin haka, abin da Allah ya haɗa, kada mutum yă raba.”
Ya amsa ya ce, “Duk wanda ya saki matarsa, ya auri wata, yana da laifin aikata zina a kan matar da ya saki.