52 Maƙiyana suna farauta ta ba dalili kamar tsuntsu.
52 “Waɗanda suke maƙiyana ba dalili Sun farauce ni kamar tsuntsu.
Kada ka bar maƙaryatan nan, su yi farin ciki a kaina; kada ka bar waɗanda suke ƙina ba dalili, su ji daɗin baƙin cikina.
Da yake sun ɓoye tarko domina ba dalili kuma babu dalili suka haƙa mini rami,
Amma wannan ya faru ne domin a cika abin da yake a rubuce cikin Dokarsu cewa, ‘Sun ƙi ni ba dalili.’
Sai Irmiya ya ce wa Sarki Zedekiya, “Wane laifi na yi maka ko fadawanka ko kuwa wannan mutane, da ka sa aka jefa ni cikin kurkuku?
Masu mulki suna tsananta mini ba dalili, amma zuciyata na rawan jiki game da maganarka.
Da kalmomin ƙiyayya sun kewaye ni; sun tasar mini ba dalili.
Waɗanda suke ƙina ba dalili sun fi gashin kaina yawa; da yawa ne abokan gābana babu dalili, su da suke nema su hallaka ni. An tilasta mini in mayar da abin da ban sata ba.
A wurin Ubangiji ne nake samun mafaka. Yaya za ku ce mini, “Ka yi firiya kamar tsuntsu zuwa duwatsu.
Mun tsira kamar tsuntsu daga tarkon mai farauta; an tsinke tarko, muka kuwa tsira.
Abin da nake gani yana kawo mini baƙin ciki domin dukan matan birnina.