28 Bari yă zauna shiru shi kaɗai, gama haka Ubangiji ya sa yă yi.
28 Bari ya zauna a kaɗaice, ya yi shiru Sa'ad da yake da damuwa.
Ban taɓa zauna a cikin ’yan tawaye ba, ban taɓa yi murna da su ba; na zauna ni kaɗai domin hannunka yana a kaina ka kuma sa na cika da haushi.
Dattawan Diyar Sihiyona sun zauna shiru a ƙasa; suka kuma sa rigar buhu. ’Yan matan Urushalima suka sunkuyar da kawunansu ƙasa.
Na kwanta a faɗake; na zama kamar tsuntsun da yake shi kaɗai a kan rufin ɗaki.
Na yi shiru; ba zan buɗe bakina ba, gama kai ne wanda ka aikata wannan.
Yana da kyau mutum yă sha wuya tun yana yaro.
“Ko a yau, ina kuka mai zafi; hannunsa yana da nauyi duk da nishin da nake yi.
Ka ɗauke bulalarka daga gare ni; na ji jiki ta wurin bugun da hannunka ya yi mini.