20 Na tuna su sosai, sai kuma na ji ba daɗi a raina.
20 Kullum raina yana tunanin azabaina, Raina kuwa ya karai.
Me ya sa kake baƙin ciki, ya raina? Me ya sa ka damu a cikina? Ka dogara ga Allah, gama zai sāke yabe shi, Mai Cetona da kuma Allahna.
Me ya sa kake baƙin ciki, ya raina? Me ya sa ka damu a cikina? Ka dogara ga Allah, gama zai sāke yabe shi, Mai Cetona da Allahna.
Lokacin da na yi tunanin wannan, sai in ji tsoro; jikina yă fara rawa.
Ubangiji yakan ba wa makafi ido, Ubangiji yakan ɗaga waɗanda aka rusunar da su ƙasa, Ubangiji yana ƙaunar masu adalci.
An kai mu ƙasa zuwa ƙura; jikunanmu sun manne da ƙasa.
Sa’ad da alhini ya yi yawa a cikina, ta’aziyyarka ta kawo farin ciki wa raina.