42 Kashegari mutanen Shekem suka tafi gonaki, aka kuwa gaya wa Abimelek.
42 Kashegari mutanen Shekem suka tafi saura, sai aka faɗa wa Abimelek.
Abimelek ya zauna a Aruma, Zebul kuwa ya kori Ga’al da ’yan’uwansa daga Shekem.
Saboda haka ya ɗauki mutanensa, ya raba su ƙungiya uku, sa’an nan ya yi kwanto a gonakin. Sa’ad da ya ga mutanen suna fitowa daga birni, sai ya yi wuf ya fāɗa musu.