44 Sai ya dinga yin wa’azi a majami’un Yahudiya.
44 Sai ya yi ta yin wa'azi a majami'un ƙasar Galili.
Yesu ya zazzaga dukan Galili, yana koyarwa a cikin majami’unsu, yana wa’azin labari mai daɗi na mulkin sama, yana kuma warkar da kowace cuta da rashin lafiyar mutane.
Sai ya tafi ko’ina a Galili, yana wa’azi a majami’unsu, yana kuma fitar da aljanu.
Ya yi ta koyarwa a majami’unsu, kowa kuwa ya yabe shi.
Wata rana, Yesu yana tsaye a bakin Tafkin Gennesaret, mutane kuma suna ta matsawa kewaye da shi, domin su ji maganar Allah,