19 In yi shelar shekarar tagomashin Ubangiji.”
19 In yi shelar zamanin samun karɓuwa ga Ubangiji.”
don in yi shelar shekarar tagomashin Ubangiji da kuma ranar ɗaukan fansar Allahnmu, don in ta’azantar da dukan waɗanda suke makoki,
Gama ranar ɗaukan fansa tana a cikin zuciyata, kuma shekarar fansata ta zo.
kuma ya ce, “In ke, ko ke ɗin ma, dā ma kin san abin da zai kawo miki salama a wannan rana, amma yanzu an ɓoye shi daga idanunki.
A matsayinmu na abokan aikin Allah, muna roƙonku kada ku karɓi alherin Allah a banza.
Sa’ad da Shekara ta Murnar Isra’ilawa ta kewayo, za a haɗa gādonsu da na kabilan mutanen da suka aura, a kuma ba su mallakar gādon da aka ɗebe daga kabilar kakanninmu.”
“Ga bawana, wanda na ɗaukaka, zaɓaɓɓen nan nawa wanda nake jin daɗi; Zan sa Ruhuna a cikinsa zai kuwa kawo adalci ga al’ummai.