16 Amma ba a ba su ikon gane shi ba.
16 Amma idanunsu a rufe, har ba su gane shi ba.
Da sassafe, sai ga Yesu tsaye a gaci, amma almajiran ba su gane cewa Yesu ne ba.
Da ta faɗin haka, sai ta juya ta ga Yesu tsaye, sai dai ba tă gane cewa Yesu ne ba.
Sa’an nan idanunsu suka buɗe, suka gane shi. Sai ya ɓace musu.
Daga baya Yesu ya bayyana a wani kamanni dabam ga biyunsu, yayinda suke tafiya ƙauye.
Da suna magana, kuma suna tattauna waɗannan abubuwa da junansu, sai Yesu da kansa ya zo yana tafiya tare da su.
Sai ya tambaye, su ya ce, “Mene ne kuke tattaunawa da juna a cikin tafiyarku?” Suka tsaya shiru, da damuwa a fuskarsu.
Ko da yake Yusuf ya gane ’yan’uwansa, su ba su gane shi ba.