21 Amma hannun wanda zai ci amanata, yana cin abincin tare da ni.
21 Amma ga shi, mai bashe ni ɗin nan yana ci a akushi ɗaya da ni.
Har abokina na kurkusa, wanda na amince da shi, wanda muke cin abinci tare, ya juya yana gāba da ni.
Yesu ya amsa ya ce, “Shi ne wanda zan ba shi gutsurin burodin nan sa’ad da na tsoma cikin kwanon.” Da ya tsoma gutsurin burodin, sai ya ba wa Yahuda Iskariyot, ɗan Siman.
Duk abokaina sun yashe ni; waɗanda nake ƙauna sun zama ba sa ƙaunata.
Da yamma ta yi, sai Yesu ya zo tare da Sha Biyun.