39 Sai waɗansu malaman dokoki suka amsa suka ce, “Ka faɗi daidai, malam!”
39 Sai waɗansu malaman Attaura suka amsa suka ce, “Malam, ka faɗi daidai.”
Aka yi babbar hayaniya. Waɗansu daga cikin malaman dokokin da suke Farisiyawa suka miƙe tsaye suka yi gardama mai ƙarfi suna cewa, “Ba mu sami wani laifi a wurin mutumin nan ba. A ce wani ruhu ko mala’ika ne ya yi masa magana fa?”
Shi ba Allah na matattu ba ne, amma na masu rai ne, gama a gare shi, duka na da rai.”
Kuma ba wanda ya sami ƙarfin halin yin masa waɗansu tambayoyi.