30 Gama idanuna sun ga cetonka,
30 Don na ga cetonka zahiri,
Dukan ’yan Adam kuwa za su ga ceton Allah!’ ”
ya ce, “Ɗan ƙaramin abu ne ka zama bawana don ka maido da kabilar Yaƙub ka kuma dawo da waɗannan na Isra’ilawan da na kiyaye. Zan kuma mai da kai haske ga Al’ummai, don ka kawo cetona zuwa iyakokin duniya.”
Ubangiji zai nuna hannunsa mai tsarki a fili a idanun dukan al’ummai, da kuma dukan iyakokin duniya za su gani ceton Allahnmu.
“Ina zuba ido ga cetonka, ya Ubangiji.
Ina jiran cetonka, ya Ubangiji, ina kuma bin umarnanka.
Ina marmarin cetonka, ya Ubangiji, dokarka kuwa ita ce farin cikina.
wanda ka shirya a gaban dukan mutane,
“Saboda haka na so ku san cewa an aika da ceton Allah ga Al’ummai, za su kuwa saurara!”