41 “Me kake so in yi maka?” Sai ya amsa ya ce, “Ubangiji, ina so in sami ganin gari.”
41 “Me kake so in yi maka?” Ya ce, “Ya Ubangiji, in sami gani!”
Kada ku damu game da kome sai dai a cikin abu duka, ku gabatar da roƙe-roƙenku ga Allah ta wurin addu’a da roƙo, tare da godiya.
Amma in muna begen abin da ba mu riga mun samu tukuna ba, mukan jira da haƙuri.
Sai Yesu ya tsaya, ya ba da umarni a kawo mutumin wurinsa. Da ya zo kusa, Yesu ya tambaye shi ya ce,
Yesu ya ce masa, “Ka sami ganin garinka; bangaskiyarka ta warkar da kai.”