Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Irmiya 23:33 - Sabon Rai Don Kowa 2020

33 “Sa’ad da waɗannan mutane, ko annabi ko firist, ya tambaye ka, ‘Mece ce maganar Ubangiji?’ Ka ce musu, ‘Wace magana? Zan yashe ku, in ji Ubangiji.’

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Littafi Mai Tsarki

33 “Kai Irmiya, sa'ad da wani mutum daga cikin mutanen nan, ko annabi, ko firist ya tambaye ka cewa, ‘Mece ce nawayar Ubangiji?’ Sai ka ce masa, ‘Ku ne nawayar, zan kuwa rabu da ku,’ ni Ubangiji na faɗa.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Irmiya 23:33
19 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Annabci, wannan ita ce maganar Ubangiji ga Isra’ila ta wurin Malaki.


Jawabi game da Ninebe a littafin wahayin Nahum, mutumin Elkosh.


Ko da sun yi renon ’ya’ya, zan sa su yi baƙin cikin kowannensu. Kaitonsu sa’ad da na juya musu baya!


“Zan yashe gidana, in rabu da gādona; Zan ba da wadda nake ƙauna a hannuwan abokan gābanta.


Abubuwan da Allah ya yi magana a kai game da Babilon da Ishaya ɗan Amoz ya gani.


Sun riƙa ce mini, “Ina maganar Ubangiji take? Bari tă cika yanzu!”


Wannan abin da Allah ya yi magana ya zo ne a shekarar da Sarki Ahaz ya mutu.


Ya fita ya je ya sadu da Asa ya kuma faɗa masa, “Ka saurare ni, Asa da kuma dukan Yahuda da Benyamin. Ubangiji yana tare da ku sa’ad da kuke tare da shi. In kuka neme shi, za ku same shi, amma in kuka yashe shi, zai yashe ku.


Annabci. Maganar Ubangiji tana gāba da ƙasar Hadrak za tă kuma sauko a kan Damaskus, gama idanun dukan mutane da na kabilan Isra’ila suna a kan Ubangiji,


Saboda haka Ubangiji ya ce, “Zan shafe Yahuda ma kamar yadda na shafe Isra’ila, daga gabana, zan ƙi Urushalima birnin da na zaɓa, da wannan haikali wanda na ce, ‘A can Sunana zai kasance.’ ”


Ana ce da su azurfar da aka ƙi, gama Ubangiji ya ƙi su.”


Zan kore ku daga gabana, kamar yadda na yi ga dukan ’yan’uwanku, mutanen Efraim.’


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ