6 Musa da Haruna suka aikata yadda Ubangiji ya umarce su.
6 Musa da Haruna suka yi yadda Ubangiji ya umarce su.
Za ka faɗi kome da na umarce ka, ɗan’uwanka Haruna kuwa zai faɗa wa Fir’auna, yă bar Isra’ilawa su fita daga ƙasarsa.
Sai Musa da Haruna suka tafi wurin Fir’auna, suka yi yadda Ubangiji ya umarce su. Haruna ya jefa sandansa ƙasa, a gaban Fir’auna da bayinsa, sai sandan ya zama maciji.
Nuhu ya yi kome kamar yadda Allah ya umarce shi.
Ku abokaina ne, in kun yi abin da na umarta.
In kuka yi biyayya da umarnaina, za ku kasance a cikin ƙaunata, kamar dai yadda na yi biyayya da umarnan Ubana na kuma kasance a cikin ƙaunarsa.
Ka shimfiɗa farillan da dole a yi biyayya da su.
Musa ya aikata dukan kome yadda Ubangiji ya umarce shi.
Musa ya duba aikin, sai ya ga cewa sun yi shi daidai yadda Ubangiji ya umarta. Sai Musa ya sa musu albarka.
Isra’ilawa suka tafi suka yi yadda Ubangiji ya umarci Musa da Haruna.
ta wurin zuriyarka kuma dukan al’umman duniya za su sami albarka, domin ka yi mini biyayya.”
Nuhu ya aikata duk abin da Ubangiji ya umarce shi.
Musa da Haruna suka yi yadda Ubangiji ya umarta. Ya ɗaga sandansa a gaban Fir’auna da bayinsa, ya bugi ruwan Nilu, dukan ruwan kuwa ya zama jini.