5 Nuhu ya aikata duk abin da Ubangiji ya umarce shi.
5 Nuhu kuwa ya yi dukan abin da Ubangiji ya umarce shi.
Nuhu ya yi kome kamar yadda Allah ya umarce shi.
Ya amsa ya ce, “Mahaifiyata da ’yan’uwana, su ne waɗanda suke jin maganar Allah, suna kuma aikata ta.”
Da ba zan sha kunya ba sa’ad da na lura da dukan umarnanka.
Ta haka aka gama dukan aikin tabanakul da Tentin Sujada. Isra’ilawa suka yi kome yadda Ubangiji ya umarci Musa.
Ko da yake shi ɗa ne, ya yi biyayya ta wurin shan wahala
Aka kuma same shi a kamannin mutum, ya ƙasƙantar da kansa ya kuma zama mai biyayya wadda ta kai shi har mutuwa, mutuwar ma ta gicciye!
Yanzu da kuka san waɗannan abubuwa, ku masu albarka ne, in kuka yi su.
Yesu ya amsa ya ce, “Bari yă zama haka yanzu; ya dace mu yi haka don mu cika dukan adalci.” Sa’an nan Yohanna ya yarda.
Musa ya aikata dukan kome yadda Ubangiji ya umarce shi.
Sai mahaifiyarsa ta ce wa bayin, “Ku yi duk abin da ya faɗa.”
Musa da Haruna suka aikata yadda Ubangiji ya umarce su.
Dabbobi da kowane abu mai rai da suka shiga ciki, namiji ne da ta mace, yadda Allah ya umarci Nuhu. Sa’an nan Ubangiji ya kulle jirgin daga baya.