6 Sai matan nan biyu masu hidima da ’ya’yansu suka matso kusa suka durƙusa.
6 Sai kuyangin suka matso kusa, su da 'ya'yansu, suka sunkuya ƙasa.
Sa’an nan Isuwa ya ɗaga ido ya ga mata da ’ya’ya. Ya yi tambaya, “Su wane ne waɗannan tare da kai?” Yaƙub ya amsa, “Su ne ’ya’yan da Allah cikin alheri ya ba bawanka.”
Biye da su, Liyatu da ’ya’yanta suka zo suka rusuna. A ƙarshe duka, sai Yusuf da Rahila suka zo, su ma suka rusuna.