22 Sai Allah ya tuna da Rahila; ya saurare ta ya kuma buɗe mahaifarta.
22 Allah kuwa ya tuna da Rahila, ya saurare ta, ya buɗe mahaifarta.
Sa’ad da Ubangiji ya ga ba a ƙaunar Liyatu, sai ya buɗe mahaifarta, amma Rahila ta zama bakararriya.
Amma Allah ya tuna da Nuhu da dukan namun jeji da dabbobin da suke tare da shi a cikin jirgi, ya kuma aika da wata iska ta hura dukan duniya, ruwan kuwa ya janye.
Yakan zaunar da matar da ba haihuwa a gidanta ta zama kamar mahaifiyar ’ya’ya mai farin ciki. Yabi Ubangiji.
Yaƙub ya fusata da ita ya ce, “Ina a matsayin Allah ne wanda ya hana ke samun ’ya’ya?”
’Ya’ya maza gādo ne daga Ubangiji, yara lada ne daga gare shi.
Ya tuna da alkawarinsa mai tsarki da ya ba wa bawansa Ibrahim.
Ishaku ya yi addu’a ga Ubangiji a madadin matarsa, saboda ba ta haihuwa. Ubangiji ya amsa addu’arsa, matarsa Rebeka kuwa ta yi ciki.
Daga baya ta haifi ’ya ta kuwa ba ta suna Dina.
’Ya’yan Rahila maza su ne, Yusuf da Benyamin.