21 Daga baya ta haifi ’ya ta kuwa ba ta suna Dina.
21 Daga baya ta haifi 'ya mace, ta kuwa raɗa mata suna Dinatu.
Waɗannan su ne ’ya’yan Liyatu maza da ta haifa wa Yaƙub a Faddan Aram, ban da ’yarsa Dina. ’Ya’yansa maza da mata duka, mutum talatin da uku ne.
Suka kashe Hamor da ɗansa Shekem da takobi, suka ɗauko Dina daga gidan Shekem suka tafi.
Sai Liyatu ta ce, “Allah ya ba ni kyauta mai daraja. A wannan lokaci mijina zai darajarta ni, domin na haifa masa ’ya’ya maza shida.” Saboda haka ta ba shi suna Zebulun.
Sai Allah ya tuna da Rahila; ya saurare ta ya kuma buɗe mahaifarta.