Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Esta 6:13 - Sabon Rai Don Kowa 2020

13 Ya je ya faɗa wa matarsa Zeresh, da dukan abokansa, me ya same shi. Masu ba shi shawara, da matarsa Zeresh, suka ce masa, “Idan Mordekai, wanda ka fara fāɗuwa a gabansa, daga zuriyar Yahudawa yake, to, ba za ka yi nasara a kansa ba, tabbatacce za ka fāɗi a gabansa!”

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Littafi Mai Tsarki

13 Da ya koma gida, sai ya faɗa wa Zeresh, matarsa, da dukan abokansa, duk abin da ya same shi. Sai mutanensa masu hikima da Zeresh, matarsa, suka ce masa, “Idan Mordekai, wanda ka fara faɗuwa a gabansa, in dai daga zuriyar Yahudawa yake, to, ba za ka yi nasara a kansa ba, amma hakika za ka fāɗi a gabansa.”

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Esta 6:13
16 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Duk wanda ya yi tafiya marar abin zargi zai zauna lafiya, amma duk wanda hanyoyinsa mugaye ne zai fāɗi nan da nan.


Wane ne yake da hikima? Zai gane waɗannan abubuwa. Hanyoyin Ubangiji daidai ne; masu adalci sukan yi tafiya a kansu, amma ’yan tawaye sukan yi tuntuɓe a kansu.


Da safe sai hankalinsa ya tashi, saboda haka sai ya aika a kawo dukan masu duba da masu hikima na Masar. Fir’auna ya faɗa musu mafarkansa, amma babu wanda ya iya ba shi fassararsu.


Cikin kwana uku, Fir’auna zai fid da kai, yă rataye ka a kan itace. Tsuntsaye kuwa za su ci naman jikinka.’ ”


Wannan ya sa sarki ya fusata ƙwarai, ya ba da umarni a tafi da dukan masu hikima na Babilon a kashe su.


“Na ji abubuwa da yawa kamar waɗannan; dukanku ba ku iya ta’aziyya ba!


Ɓacin rai da baƙin ciki sun cika shi, kamar sarkin da yake shirin yaƙi,


Sai bawan ya faɗa wa Ishaku duk abin da ya yi.


Kamar zaki sun laɓe sun kwanta, kamar zakanya, wa zai yi ƙarfin hali yă tashe su? “Bari waɗanda suka albarkace ka, su sami albarka waɗanda kuma suka la’anta ka, su la’antu!”


A cikin hamada ya same shi, a jeji marar amfani, inda namomi suke kuka. Ya tsare shi, ya kuma lura da shi; ya bi da shi kamar ƙwayar idonsa,


“Kada ku taɓa shafaffena; kada ku yi wa annabawa lahani.”


Ubangiji zai gāji Yahuda a matsayin rabonsa a cikin ƙasa mai tsarki zai kuma sāke zaɓi Urushalima.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ