28 “Amma yanzu ku dube ni da kyau, zan yi muku ƙarya ne?
28 Ku dubi fuskata, Lalle ba zan faɗi ƙarya ba.
Abin da zan faɗa gaskiya ne daga cikin zuciyata; bakina zai faɗi gaskiyar abin da na sani.
bakina ba zai faɗi mugun abu ba, harshena kuma ba zai yi ƙarya ba.
Ku kuma kun ishe ni da ƙarairayi; ku likitocin wofi ne, dukanku!
Abin da zan gaya maka ba ƙarya ba ne; mai cikakken sani yana tare da kai.
Ko maganganun nan naka marasa amfani za su sa mutane su yi maka shiru? Ba wanda zai kwaɓe ka lokacin da kake faɗar maganar da ba daidai ba?
“In wannan ba haka ba ne, wane ne zai shaida ƙarya nake yi har yă ƙi yarda da maganata?”