5 “Ayuba ya ce, ‘Ba ni da laifi, amma Allah ya hana mini hakkina.
5 Gama Ayuba ya ce, ‘Ni marar laifi ne, Amma Allah ya ƙwace mini halaliyata.
‘ni mai tsarki ne marar zunubi; ina da tsabta kuma ba ni da laifi.
“Na rantse da Allah mai rai, wanda ya danne mini gaskiyata, Maɗaukaki, wanda ya sa nake cikin ɗacin rai.
Sai mutanen nan uku suka daina amsa wa Ayuba, domin a ganinsa shi mai adalci ne.
Na yafa adalci ya zama suturata; gaskiya ita ce rigata da rawanina.
duk da haka hannuwana ba su aikata ɓarna ba kuma addu’ata mai tsabta ce.
Ka ce wa Allah, ‘Abin da na gaskata ba laifi ba ne kuma ni mai tsabta ne a gabanka.’
Ko da yake ka san ba ni da laifi, kuma ba wanda zai iya cetona daga hannunka.
Zai sa hadari yă danne ni yă ƙara mini ciwona ba dalili.
Ku bi a hankali, kada ku ɗora mini laifi; ku sāke dubawa, gama ba ni da laifi.
Yanzu da na shirya ƙarata, na san za a ce ba ni da laifi.
Bari mu zaɓi abin da yake daidai, bari mu koyi abin da yake mai kyau tare.
Ya Yaƙub, ya Isra’ila, me ya sa kake ce kana kuma gunaguni cewa, “Hanyata tana a ɓoye daga Ubangiji; Allah bai kula da abin da yake damuna ba”?
Allah ba mai shari’ar gaskiya ba ne? Ko Maɗaukaki yakan yi abin da ba daidai ba?
“Ko da yake na yi kuka cewa, ‘An yi mini ba daidai ba!’ Ba a amsa mini ba; ko da yake na nemi taimako, ba a yi adalci ba.