10 Duk da haka Allah ya same ni da laifi; ya ɗauke ni maƙiyinsa,
10 Ka ce Allah ya zarge ka ya ɗauke ka tankar maƙiyansa,
Yana jin haushina ya lissafta ni cikin maƙiyansa.
“Ayuba ya ce, ‘Ba ni da laifi, amma Allah ya hana mini hakkina.
(“Kash, da ina da wanda zai ji ni! Na sa hannu ga abin da na faɗa don kāre kaina, bari Maɗaukaki yă amsa mini; bari mai tuhumata da laifi yă yi ƙarata a rubuce.
Ka dube ni ba tausayi; Ka kai mini hari da ƙarfin hannunka.
Allah ya kai mini hari ya yi kaca-kaca da ni cikin fushinsa yana cizon haƙoransa don fushin da yake yi da ni; ya zura mini ido.
Ba shakka a lokacin ne za ka lura da matakaina amma ba za ka kula da zunubaina ba.
Zai sa hadari yă danne ni yă ƙara mini ciwona ba dalili.
duk da haka ina tsoron duk wahalata, domin na san ba za ka ɗauke ni marar laifi ba.
Tun da an riga an ɗauke ni mai laifi, duk ƙoƙarina a banza yake.