17 Ni ma zan faɗi nawa; ni ma zan faɗi abin da na sani.
17 A'a, ni kuma zan ba da tawa amsa, In kuma faɗi ra'ayina.
“Amma na gaya maka, a nan ba ka yi daidai ba, gama Allah ya fi mutum girma.
“Saboda haka nake ce muku, ku saurare ni; ni ma zan gaya muku abin da na sani.
Dole ne in jira yanzu da suka yi shiru, yanzu da suke tsaye a wurin ba su da amsa.
Gama ina cike da magana, kuma ruhun da yake cikina yana iza ni;