20 “To, daga ina ke nan hikima ta fito? Ina fahimta take zama?
20 “To, daga ina hikima ta fito? A wane wuri kuma haziƙanci yake?
In waninku ya rasa hikima, ya kamata yă roƙi Allah, mai bayarwa hannu sake ga kowa ba tare da gori ba, za a kuwa ba shi.
Amma a ina ne za a iya samun hikima? Ina fahimta take zama?
Kowane abu mai kyau da kuma kowace cikakkiyar kyauta daga sama suke, sun sauko ne daga wurin Uban haskoki, wanda ba sauyawa ko wata alamar sākewa a gare shi faufau.
Ya kuma ce wa mutum, ‘Tsoron Ubangiji shi ne hikima, kuma guje wa mugunta shi ne fahimi.’ ”
Allah ya gane hanyar zuwa wurinta. Shi ne kaɗai ya san inda take zama,
Gama Ubangiji yana ba da hikima, daga bakinsa kuma, sani da ganewa sukan fito.
An ɓoye ta daga idanun kowane abu mai rai, har tsuntsayen sararin sama ma an ɓoye masu ita.