3 Muddin ina da rai a cikina kuma numfashin Allah yana cikin hancina,
3 Muddin ina numfashi, Ruhun Allah kuma yana cikin hancina
Sa’an nan Ubangiji Allah ya yi mutum daga turɓayar ƙasa, ya kuma hura numfashin rai cikin hancinsa, mutumin kuwa ya zama rayayyen taliki.
Ruhun Allah ne ya yi ni; numfashin Maɗaukaki ya ba ni rai.
Ku daina dogara ga mutum, wanda numfashi ne kawai yake da shi a hancinsa. Wace daraja gare shi?
Amma ruhun da yake cikin mutum, numfashin Maɗaukaki shi ne yake ba shi ganewa.
Ba a kuma yin masa hidima da hannun mutum, sai ka ce mai bukatan wani abu, domin shi kansa ne ke ba wa dukan mutane rai da numfashi da kuma kome.
Ran kowace halitta yana a hannunsa, haka kuma numfashin dukan ’yan adam.