4 Zan kai damuwata wurinsa in yi gardama da shi.
4 Da zan kai ƙarata a gare shi, in faɗa masa duk muhawarata, in kāre kaina ne.
Yanzu da na shirya ƙarata, na san za a ce ba ni da laifi.
Ku tunashe ni abin da ya riga ya wuce, bari mu yi muhawwara wannan batu tare; ku kawo hujjarku na nuna rashin laifinku.
Ka nuna ni marar laifi ne, ya Allah, ka kuma nemi hakkina a kan al’ummai marasa sanin Allah. Ka kuɓutar da ni daga masu ruɗu da mugayen mutane.
Saboda sunanka, ya Ubangiji, ka gafarta laifina, ko da yake mai girma ne.
“Gaya mana abin da ya kamata mu ce masa; ba za mu iya kawo ƙara ba domin duhunmu.
Amma ka riga ka faɗa, ‘Tabbatacce zan sa ka yi albarka. Zan kuma sa zuriyarka su zama kamar yashin teku da ba a iya ƙirgawa.’ ”
Amma ina so in yi magana da Maɗaukaki, in kai kukana wurin Allah kai tsaye.
Da a ce na san inda zan same shi; da a ce zan iya zuwa wurin da yake zama!
Zan nemi in san abin da zai ce mini, in kuma auna abin da zai ce mini.
“Mai neman sa wa wani laifi zai iya ja da Maɗaukaki? Bari mai tuhumar Allah yă amsa masa.”