3 Da a ce na san inda zan same shi; da a ce zan iya zuwa wurin da yake zama!
3 Da ma na san inda zan same shi, In kuma san yadda zan kai wurinsa,
a madadin mutum ya yi roƙo ga Allah kamar yadda mutum yakan yi roƙo domin abokinsa.
Amma ina so in yi magana da Maɗaukaki, in kai kukana wurin Allah kai tsaye.
Har yanzu dai da sauran dama domin waɗansu su shiga, su kuwa waɗanda aka fara yi wa albishirin nan sun kāsa shiga saboda rashin biyayya.
Ko da yake zunubanmu suna ba da shaida a kanmu, Ya Ubangiji, ka yi wani abu saboda sunanka. Gama jan bayanmu ya yi yawa; mun yi maka zunubi.
I, Ubangiji, cikin tafiya a hanyar dokokinka, muna sa zuciya gare ka; sunanka da tunani a kanka su ne marmarin zukatanmu.
“Ko a yau, ina kuka mai zafi; hannunsa yana da nauyi duk da nishin da nake yi.
Zan kai damuwata wurinsa in yi gardama da shi.
Shi mai yin roƙo a madadina abokina ne yayinda nake kuka ga Allah;
Tabbatacce kai ne Allah wanda ya ɓoye kanka, Ya Allah da Mai Ceton Isra’ila.