32 Za a bizne shi a kabari, a kuma yi tsaron kabarinsa.
32 Sa'ad da aka ɗauke shi zuwa hurumi, A inda ake tsaron kabarinsa,
“Ana nan, sai mai baran ya mutu, kuma mala’iku suka ɗauke shi zuwa gefen Ibrahim. Mai arzikin ma ya mutu, aka kuma binne shi.
Kamar tumaki an ƙaddara su ga kabari; za su kuwa zama abincin mutuwa amma masu gaskiya za su yi mulki a kansu da safe. Kamanninsu za su ruɓe a cikin kabari, nesa da gidajensu masu tsada.
Wane ne yake gaya masa abin da ya yi? Wane ne yake rama abin da ya yi?
Akan mai da ƙasa a kan gawarsa a hankali; dukan jama’a suna binsa, da yawa kuma suna gabansa.
Amma za ku mutu kamar mutum kurum; za ku fāɗi kamar duk wani mai mulki.”