21 Ko zai damu da iyalin da ya bari a baya sa’ad da kwanakinsa suka ƙare?
21 Bayan rasuwar mutum, Ruwansa ne ya sani ko 'ya'yansa suna jin daɗi?
An lissafta kwanakin mutum; ka riga ka ɗibar masa watanni, ka yi masa iyaka, ba zai iya wuce iyakar ba.
Sai na ce, “Kada ka ɗauke ni a tsakiyar kwanakina, ya Allah; shekarunka suna bi cikin dukan zamanai.
Amma kai, ya Allah, za ka kawar da mugaye zuwa cikin ramin lalacewa; masu kisa da mutane masu ruɗu ba za su kai rabin kwanakin rayuwarsu ba. Amma ni dai, na dogara gare ka.
Ko an martaba ’ya’yansa maza, ba zai sani ba; Ko an wulaƙanta su, ba zai gani ba.
Bari idanunsa su ga yadda zai hallaka; bari yă sha daga fushin Maɗaukaki.
“Wani zai iya koya wa Allah ilimi tun da yana shari’anta har da waɗanda suke manya masu iko?