17 duk da haka hannuwana ba su aikata ɓarna ba kuma addu’ata mai tsabta ce.
17 Amma ban yi wani aikin kama-karya ba, Addu'ata ga Allah kuwa ta gaskiya ce.
Ubangiji yana ƙyamar hadayar mugaye, amma addu’ar masu aikata gaskiya kan sa ya ji daɗi.
Bari kowane mutum da dabba yă yafa rigunan makoki. Kowa yă roƙi Allah da gaske, kowa kuma yă bar mugayen ayyukan da yake yi.
Yanar gizo-gizonsu ba amfani don tufa; ba za su iya rufuwa da abin da suka yi ba. Ayyukansu mugaye ne, ayyukan tā da hargitsi kuma suna a hannuwansu.
Gama marasa tsoron Allah za su zama marasa ba da ’ya’ya, wuta kuma za tă ƙona tenti na masu son cin hanci.
Dukan kwanakin ransa mugu yana shan wahala, wahala kaɗai zai yi ta sha.
in ka kawar da zunubin da yake hannunka, ba ka bar zunubi ya kasance tare da kai ba
Ina so maza a ko’ina su ɗaga hannuwansu masu tsarki cikin addu’a, ba tare da fushi ko faɗa ba.
“Ya duniya, kada ki ɓoye jinina; bari yă yi kuka a madadina!
bakina ba zai faɗi mugun abu ba, harshena kuma ba zai yi ƙarya ba.
‘ni mai tsarki ne marar zunubi; ina da tsabta kuma ba ni da laifi.
Ka ji, ya Ubangiji, roƙona na adalci; ka saurari kukata. Ka kasa kunne ga addu’ata, ba ta fitowa daga leɓuna masu ƙarya.