6 Ku ji gardamata yanzu; ku ji roƙon da zai fito daga bakina.
6 “Ku saurara mini, zan faɗi ƙarata.
“Ku ji maganata, ku masu hikima; ku saurare ni, ku masu ilimi.
Sa’ad da aka gaya wa Yotam wannan, sai ya hau Dutsen Gerizim ya yi kira da ƙarfi ya ce, “Ku saurare ni, ’yan ƙasar Shekem, don Allah yă saurare ku.
In da za ku yi shiru gaba ɗaya! Zai zama muku hikima.
Za ku iya yin muguwar magana a madadin Allah? Ko za ku yi ƙarya a madadinsa?
Ku saurara da kyau ku ji abin da zan faɗa; bari kunnuwanku su ji abin da zan ce.