17 Ku saurara da kyau ku ji abin da zan faɗa; bari kunnuwanku su ji abin da zan ce.
17 Sai a saurari bayanin da zan yi.
“Amma yanzu, Ayuba, ka saurari abin da zan ce; ka sa hankali ga kowane abin da zan faɗa.
“Ku saurare ni da kyau; bari wannan yă zama ta’aziyyar da za ku ba ni.
Ku ji gardamata yanzu; ku ji roƙon da zai fito daga bakina.
lalle wannan zai kawo mini kuɓuta gama ba wani marar tsoron Allah da zai iya zuwa wurinsa!
Yanzu da na shirya ƙarata, na san za a ce ba ni da laifi.
(“Kash, da ina da wanda zai ji ni! Na sa hannu ga abin da na faɗa don kāre kaina, bari Maɗaukaki yă amsa mini; bari mai tuhumata da laifi yă yi ƙarata a rubuce.