10 Ba shakka zai kwaɓe ku in kun nuna sonkai a ɓoye.
10 Ko da yake kun ɓoye son zuciyarku, Duk da haka zai tsauta muku,
Amma in kuka nuna bambanci, kun yi zunubi ke nan shari’a kuma ta same ku da laifi a matsayin masu karya doka.
“Har yaushe za ku kāre marasa adalci ku kuma goyi bayan mugaye? Sela
Ko za ku nuna masa sonkai? Ko za ku yi gardama a madadinsa?
Ba zan nuna wa wani sonkai ba, ko kuma in yi wa wani daɗin baki ba;
wanda ba ya nuna sonkai ga ’ya’yan sarki kuma ba ya goyon bayan masu arziki a kan matalauta, gama dukansu shi ya yi su da hannuwansa.
Yanzu fa ku ji tsoron Ubangiji. Ku yi hankali a kan abin da kuke yi, gama Ubangiji Allahnmu ba ya sonkai ko nuna wariya ko cin hanci.”