Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Ayuba 10:3 - Sabon Rai Don Kowa 2020

3 Kana jin daɗin ba ni wahala, don me ka yashe ni, abin da ka halitta da hannunka, yayinda kake murmushi game da shirye-shiryen mugaye?

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Littafi Mai Tsarki

3 Daidai ne a gare ka ka yi mugunta? Ka wulakanta abin da kai da kanka ka yi? Sa'an nan ka yi murmushi saboda dabarun mugaye?

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Ayuba 10:3
27 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Duk da haka, Ubangiji, kai ne Ubanmu. Mu yumɓu ne, kai kuma mai ginin tukwane; dukanmu aikin hannunka ne.


Ubangiji zai cika manufarsa a kaina; ƙaunarka, ya Ubangiji, madawwamiya ce har abada, kada ka ƙyale ayyukan hannuwanka.


Za ka kira zan kuwa amsa maka; za ka yi marmarin abin da hannunka ya halitta.


Saboda haka, waɗanda suke shan wahala bisa ga nufin Allah ya kamata su danƙa kansu ga Mahaliccinsu mai aminci, su kuma ci gaba da aikata abin da yake daidai.


Ubangiji yakan ji masu bukata ba ya kuwa ƙyale kamammun mutanensa.


“Ko za ka ƙi yarda da shari’ata? Za ka ba ni laifi don ka nuna kai marar laifi ne?


“Mai neman sa wa wani laifi zai iya ja da Maɗaukaki? Bari mai tuhumar Allah yă amsa masa.”


Duk da haka kuwa shi ne ya cika gidajensu da abubuwa masu kyau, saboda haka ba ruwana da shawarar mugaye.


Amma arzikinsu ba a hannunsu yake ba saboda haka ba ruwana da shawarar mugaye.


Lokacin da ƙasa ta faɗa a hannun mugaye, yakan rufe idanun masu shari’a. In ba shi ba wa zai yi wannan?


Ba bambanci; shi ya sa na ce, ‘Yana hallaka marasa laifi da kuma mugaye.’


“Ba shakka, Allah ba ya ƙin marar laifi, ko kuma yă ƙarfafa masu aikata mugunta.


“Da hannuwanka ka ƙera ni, kai ka halicce ni. Yanzu kuma kai za ka juya ka hallaka ni?


Allah ya bashe ni ga mugayen mutane, ya jefa ni hannun mugaye.


sai ku san cewa Allah ya yi mini ba daidai ba ya kewaye ni da ragarsa.


“Na rantse da Allah mai rai, wanda ya danne mini gaskiyata, Maɗaukaki, wanda ya sa nake cikin ɗacin rai.


Ka dube ni ba tausayi; Ka kai mini hari da ƙarfin hannunka.


Shi wanda ya yi ni a cikin uwata ba shi ne ya yi su ba? Ba shi ne ya yi mu a cikin uwayenmu ba?


Ruhun Allah ne ya yi ni; numfashin Maɗaukaki ya ba ni rai.


Ku san cewa Ubangiji shi ne Allah. Shi ne ya yi mu, mu kuwa nasa ne; mu mutanensa ne, tumakin makiyayarsa.


har kake fushi da Allah kake kuma faɗar waɗannan maganganu daga bakinka?


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ