2 Zan ce wa Allah, kada ka hukunta ni, amma ka gaya mini laifin da na yi maka.
2 Kada ka hukunta ni, ya Allah. Ka faɗa mini laifin da kake tuhumata da shi.
Kada ka gabatar da bawanka a gaban shari’a, gama babu wani mai rai da yake adali a gabanka.
Tun da an riga an ɗauke ni mai laifi, duk ƙoƙarina a banza yake.
Saboda haka, yanzu babu hukunci don waɗanda suke cikin Kiristi Yesu,
Amma kai, ya Ubangiji Mai Iko Duka, ka yi da ni da kyau saboda sunanka; ta alherin ƙaunarka, ka cece ni.
Kada ka tuna da zunuban ƙuruciyata da kuma hanyoyin tawayena; bisa ga ƙaunarka ka tuna da ni, gama kai nagari ne, ya Ubangiji.
Ko da mutum yana so yă yi gardama da shi, ba zai taɓa amsa masa ba ko da sau ɗaya cikin dubu.
“Mai neman sa wa wani laifi zai iya ja da Maɗaukaki? Bari mai tuhumar Allah yă amsa masa.”
In na yi zunubi, me na yi maka, kai mai lura da mutane? Don me ka sa ni a gaba? Na zame maka kaya mai nauyi ne?
Abubuwa nawa na yi waɗanda ba daidai ba, kuma zunubi ne? Ka nuna mini laifina da zunubina.
“A wurin mutum ne na kawo kukana? Don me ba zan kāsa haƙuri ba?
Don me ka yi masa gunaguni cewa ba ya amsa tambayoyin mutum?
Ka ji muryata sa’ad da na yi kira, ya Ubangiji; ka yi mini jinƙai ka kuma amsa mini.