Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Ayuba 10:15 - Sabon Rai Don Kowa 2020

15 Idan ina da laifi, kaitona! Ko da ba ni da laifi, ba zan iya ɗaga fuskata ba, gama kunya ta ishe ni duk ɓacin rai ya ishe ni.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Littafi Mai Tsarki

15 Da cewa na yi zunubi, na shiga uku ke nan a wurinka. Amma sa'ad da na yi abin kirki ba na samun yabo. Ina baƙin ciki ƙwarai, kunya ta rufe ni.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Ayuba 10:15
23 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Kaiton masu mugunta! Masifa tana a kansu! Za a rama abin da hannuwansu suka yi.


Ko da yake ba ni da laifi, ba zan iya amsa masa ba; sai dai roƙon jinƙai zan iya yi ga mahukuncina.


Za ku kuma ga bambanci tsakanin masu adalci da mugaye, tsakanin waɗanda suke wa Allah hidima da kuma waɗanda ba sa yi.


Ka dubi wahalata da kuma azabata ka ɗauke mini dukan zunubaina.


Ko da yake ka san ba ni da laifi, kuma ba wanda zai iya cetona daga hannunka.


Haka ku ma, bayan kun yi duk abin da aka ce muku ku yi, ya kamata ku ce, ‘Mu bayi ne marasa cancanta, mun dai yi aikinmu ne kaɗai.’ ”


“Duba, Ubangiji, ka ga ƙuncin da nake ciki! Ina shan azaba a raina, ba ni da kwanciyar rai a cikin zuciyata, domin na yi tawaye sosai. A waje takobi na kisa; a ciki kuma akwai mutuwa.


Sai na tā da murya na ce, “Kaitona! Na shiga uku! Gama ni mutum ne mai leɓuna marar tsarki, kuma ina raye a cikin mutane masu leɓuna marasa tsarki, idanuna kuma sun ga Sarki, Ubangiji Maɗaukaki.”


Ka dubi wahalata ka cece ni, gama ban manta da dokarka ba.


Mugaye za su koma kabari, dukan al’umman da suka manta da Allah.


“Bari maƙiyana su zama kamar mugaye, masu gāba da ni kuma su zama kamar marasa adalci.


Shi ya sa na tsorata a gabansa; sa’ad da na yi tunanin wannan duka, nakan ji tsoronsa.


Lokacin da na yi tunanin wannan, sai in ji tsoro; jikina yă fara rawa.


Tun da an riga an ɗauke ni mai laifi, duk ƙoƙarina a banza yake.


Wane ne ya isa yă hana shi in ya ƙwace abu? Wa zai ce masa, ‘Me kake yi?’


Ubangiji ya ce, “Tabbatacce na ga azabar mutanena a Masar. Na ji su suna kuka saboda matsin da shugabannin gandunsu suke musu, na kuma damu da wahalarsu.


Ku bi a hankali, kada ku ɗora mini laifi; ku sāke dubawa, gama ba ni da laifi.


Ka rushe fuskokinsu da kunya don mutane su nemi sunanka, ya Ubangiji.


saboda ba’ar waɗanda suke zagi suke kuma ƙina, saboda abokan gābana, waɗanda suka sha alwashi sai sun yi ramuwa.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ